Manyan masu ruwa da tsaki da masanan tsaron sun bayyana damuwarsu, game da jita-jitar cewar, tsohon Sarkin zai kai ziyara Kano.
Leadership ta rawaito cewa, gwamnatin jihar ta bayyana cewa, a halin yanzun ba ta da masaniya kan lamarin, ta ce, ko da gaske ne ta na maraba da zuwansa.
Masana a siyasa da tsaro sun nuna matukar damuwarsu kan shirin tsohon sarkin da ak sauke, Sanusi Lamido, na kai ziyara jahar Kano. Wasu daga cikin masu ruwa da tsaki na jiha, waÉ—an da suka zanta da jaridar Leadership, sun roki tsohon sarkin ya dakatar da shirin zuwa Kano a halin yanzu.
A cewarsu, tsoron da suke shi ne, akwai yuwar tayar da hankulan mutane wanda ka iya sanadin rikici tsakankin masoyan tsoron sarkin da ‘yan adawarsa.