fidelitybank

Daga yanzu babu wanda zai sake raina mai zaɓe a Najeriya – Buhari

Date:

Shugaba Muhammadu Buhari, ya ce, zaɓukan 2023 sun nuna yadda mulkin dimokuraɗiyya ke ci gaba da ginuwa da kuma samun karfi musamman ma ta yadda masu zaɓe suka waye da kuma sanin shugabannin da za su zaɓa.

Shugaba Buhari ya bayyana haka ne lokacin da ya karɓi bakuncin sabon Sarkin Dutse, Alhaji Muhammad Hamim Nuhu a fadarsa da ke Abuja, inda ya ce, sakamakon zaɓen gwamnoni guda 10 da suka kasa samun nasarar zuwa majalisar dattawa, ya nuna cewa yanzu babu tabbas game da samun mulki kuma yanzu masu zaɓe su ke da wuƙa da nama.

Karanta Wannan: Ɗan takarar mu Obi ake hari ba jam’iyyar mu ba – LP

“Hakan ya nuna cewa, dimokuraɗiyyar mu na ƙara girma da kuma yadda masu zaɓe suka waye. Abin da ya bani mamaki shi ne ɗan Najeriyar da aka raina, a yanzu shi ke da wuƙa da nama wajen zaɓar wanda ya dace,” in ji Buhari.

“An mayar da cewa bayan gwamna ya yi shekara takwas, daga nan zai tafi majalisar dattawa ba tare da shan wahala ba. Daga yanzu babu wanda zai sake raina mai zaɓe a Najeriya. Siyasa za ta zama abu mafi wahala nan gaba,” a cewar Buhari.

Da yake magana, sabon Sarkin na Dutse, Alhaji Muhamamd Hamim, ya gode wa gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari saboda taimaka wa jihar Jigawa ta samu ci gaba a ɓangaren noman shinkafa da amincewa da gina layin dogo daga Kano zuwa Dutse da kuma dawo da zaman lafiya a jihar

naija hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

QPC ta nemi INEC ta soke zaɓen Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Rudunar ƴansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum...

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na ɗaya daga cikin jhihohin da ake kaɗa...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...
X whatsapp