Ministan Abuja, babban birnin Najeriya, Nyesom Wike, ya ce, daga watan Janairun 2025, duka ababen hawan da ake haya da su a birnin, za su kasance jami’an ‘yansanda da DSS na da cikakkun bayansu.
Mista Wike ya bayyana hakan ne ranar Alhamis lokacin bikin raba tallafin sabbin motocin Taxi ga wasu matasa.
Ministan ya zargi wasu masu amfani da ababen hawan da kasancewa masu yi wa ‘yan bindiga leÆ™en asiri.
“Mafi yawan masu tuÆ™a Keke Napep da masu achaÉ“a masu bai wa ‘yan bindiga bayanai ne.”
“Don haka daga watan Janairun sabuwar shekara, babu wanda za mu bari ya É—auki fasinja a motarsa ba tare da samun sahalewar jami’an tsaro ba, sannan dole ya yi wa motarsa fenti”, in ji ministan.
Ya Æ™ara da cewa “ba za mu bari a sake amfani da kowace irin mota wajen É—aukar fasinja a Abuja ba”.
”Za mu É—auki bayanan direba da na motarsa, kamar sunan direba da lambar motarsa da sauran muhimman bayanai”, in ji mista Wike.