fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Ɗan majalisar Wakilai ya jikkata a taron PDP

Date:

Mutane da dama ne suka jikkata, sakamakon rikicin da ya barke a karamar hukumar Aninri da Nssuka na jihar Enugu yayin taron jam’iyyar PDP.

An tattaro cewa ‘yan barandan da suka jefa kujeru da kwalabe a Nsukka a ranar Asabar din da ta gabata sun yi amfani da makamai cikin ‘yanci a daidai lokacin da mata da wasu suka tsallake rijiya da baya a kokarin tserewa.

Wata majiya da ta nemi a sakaya sunanta ta shaida wa manema labarai cewa, batun wanda ke wakiltar al’ummar Nsukka/Igbo-Eze ta Kudu a Majalisar Wakilai, an ce shi ne ya haddasa rikicin a yayin taron.

Haka kuma a wani taron siyasa da aka gudanar a Ndeaboh a karamar hukumar Aniiri, da dama sun samu munanan raunuka yayin da wasu ke kwance a asibiti sakamakon wani mummunan hari da aka kai a yayin taron siyasa na PDP.

A martanin da ya mayar, tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Ike Ekweremadu, ya yi Allah wadai da kakkausar murya kan rikicin da ya rikide wa taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP a karamar hukumar Aninri ta jihar Enugu a karshen mako da kuma mummunan harin da aka kai wa magoya bayansa da abokan siyasarsa a yayin taron da aka ce a Ndeaboh.

Ekweremadu ya tuna cewa, harin ya bar mutane da dama ciki har da dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Aninri a majalisar dokokin jihar Enugu, Hon. Chinedu Okwu wanda ya samu munanan raunuka, kuma yana kwance a asibiti ya yi kira ga jami’an tsaro da su tabbatar an gurfanar da wadanda suka aikata laifin.

vanguard news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp