fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Ƴan ta’adda sun ƙara sakin mutanen jirgin ƙasan Kaduna

Date:

Akalla mutane bakwai da aka yi garkuwa da su daga jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja aka sako ranar 28 ga watan Maris.

Mutanen bakwai da ‘yan ta’addan suka yi garkuwa da su sun hada da iyali guda shida da mace daya.

Tukur Mamu, Mawallafin Desert Herald da ke Kaduna, kuma mai ba da shawara kan harkokin yada labarai ga wani malamin addinin Islama, Sheikh Ahmad Gumi, ya tabbatar wa manema labarai a Kaduna.

Mutanen da aka sako sun hada da Abubakar Idris Garba, matarsa, Maryam Abubakar Bobo, da kuma babban dansu, Ibrahim Abubakar Garba, mai shekaru 10.

Sauran sun hada da Fatima Abubakar Garba (7), Imran Abubakar Garba (5), da kuma Zainab Abubakar Garba, ‘yar shekara daya da rabi kacal.

Abubakar Idris Garba, ma’aikaci ne a hukumar yi wa Majalisar Dokoki ta kasa hidima, dan tsohon shugaban mulkin soja ne na jihohin Kano da Benue.

Haka kuma an saki wata mata ‘yar shekara 60, Hajiya Aisha Hassan, wacce aka ce an sake ta ne sakamakon kalubalen rashin lafiya da ke barazana ga rayuwa da ta tabarbare a kwanan nan.

news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp