fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Ƴan majalisar dokokin Oyo PDP za su sauya sheƙa zuwa APC

Date:

‘Yan majalisar dokokin jihar Oyo takwas da aka zaba a karkashin jam’iyyar PDP za su fice daga jam’iyyar.

An tattaro cewa, ‘yan majalisar da wasu jiga-jigan jam’iyyar a jihar Kudu maso Yamma sun kammala shirin komawa jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

Naija News ta tuna cewa, a baya-bayan nan ne mataimakin gwamnan jihar Oyo, Rauf Olaniyan ya fice daga jam’iyyar PDP zuwa APC, bayan da suka samu sabani da gwamna Seyi Makinde.

Makinde, wanda ke neman sake tsayawa takara a 2023, ya ki ya zabi Olaniyan a matsayin abokin takararsa.

Daya daga cikin ‘yan majalisar PDP da suka fusata ya tabbatar da cewa, wasu ‘yan majalisar na shirin ficewa daga jam’iyyar mai mulki ranar Lahadi.

Ya shaida wa Vanguard cewa, shirin sauya shekar ya kasance ne, saboda an hana ‘yan majalisar dokokin jihar tikitin tsayawa takara a zaben 2023 na PDP.

A halin da ake ciki kuma, an yi Allah wadai da Shugaban Jam’iyyar PDP na kasa, Iyorchia Ayu, da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Atiku Abubakar, kan kin kamfe na jam’iyyar a Ekiti.

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...

Wike ya caccaki Rotimi a kan jam’iyyar ADC

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya caccaki tsohon...

Tsige ni daga mukamin Wazirin Gaya ba a kan doka ba ne – Usman Alhaji

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya...

Gini mai bene uku ya danne Mutane a jihar Legas

Wani gini mai bene uku ya rufta a unguwar...

Kotu ta daure Matashi dan Tiktok da ya ke sanya rigar mama

Wata kotu a jihar Kano, ta yanke wa wani...

Peter Obi ka gaggauta ficewa daga jam’iyyar mu nan da awa 48 – Labour Party

Bangaren jam’iyyar Labour da Julius Abure ke jagoranta, ya...
X whatsapp