fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Ƴan bindiga sun sace Ango da Amarya da iyalan tsohon Kwamishina a Kaduna

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun kashe wani sabon ango tare da sace matarsa mai ciki a garin Jere da ke karamar hukumar Kagarko a jihar Kaduna.

‘Yan bindigar sun kuma yi awon gaba da wasu mutane hudu na iyalan tsohon Kwamishinan Yakin Talauci na Jihar Kaduna, Abdulrahman Ibrahim Jere.

‘Yan bindigar da suka afkawa al’ummar sun haura sama da 50, inda suka mamaye al’ummar da ke kan hanyar Abuja zuwa Kaduna a kan babura.

An ce suna shiga gida gida har sai da suka gano gidan Jere wanda aka tara kila shi ne abin da suke hari.

Ko da yake tsohon Kwamishinan ya ce, baya gida lokacin da ‘yan fashin suka ziyarci gidansa, sun yi awon gaba da matarsa da wata yarinya da kanwar sa da kuma kanwar matarsa.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna (PPRO) ASP Mohammed Jalige, bai amsa kiran da ya yi masa na mayar da martani kan harin ba, ya kuma kasa amsa kiran wayarsa da aka yi masa a lokacin mika wannan rahoton. In ji The Nation.

www nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp