Wasu ‘yan bindiga sun kashe wani mutum tare da sace ‘ya’yansa mata biyu a garin Azuba da ke jihar Nasarawa.
Marigayin mai suna Alhaji Zakari Kigbu an ce dan uwa ne ga gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule.
Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Nasarawa, ASP Ramhan Nansel, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce, “Mun samu kiran waya da misalin karfe 12:15 na safe game da harin, inda muka yi gaggawar daukar matakan da suka dace ta hanyar tattara ‘yan sintiri da sojoji zuwa wurin.
Da isar sa, an gano cewa an harbe wanda aka kashe a cikinsa.
“An garzaya da shi asibiti inda aka tabbatar da mutuwarsa.
“An sace ‘ya’yansa mata guda biyu zuwa inda ba a sani ba.
“Rundunar ta fara farautar wadanda suka aikata wannan aika aika.” In ji Independent .