fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Shugabar mata ta jam’iyyar PDP ta koma APC

Date:

Hajiya Yar-Sokoto Jega, shugabar mata ta jam’iyyar PDP mai wakiltar Kebbi ta tsakiya a jihar Kebbi, ta koma jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

Jega ta bayyana haka ne a lokacin da ta ke jawabi a wajen wani biki a Birnin Kebbi a ranar Laraba.

A cewarta, ta bar jam’iyyar ne saboda rashin adalci da kuma rashin shugabanci na gari.

Jega ta bayyana cewa ta yanke shawarar komawa jam’iyyar APC ne saboda dimbin nasarorin da Gwamna Atiku Bagudu ya samu, inda ta kara da cewa ta koma jam’iyyar ne da magoya baya sama da 800.

“Na shafe shekaru da yawa a PDP, ba su da wani abin da za su nunawa mutane kuma jam’iyyar ta yi watsi da mu.

“Ni ma ina amfani da kudina wajen tafiyar da jam’iyya, amma duk da haka ban ga wani sauyi da jama’ata ba, musamman matan da nake wakilta.

“Kafin sauya sheka na, ina shugabancin kananan hukumomi takwas a karkashin jam’iyyar PDP, na tafi tare da mafi yawan mabiyana,” in ji Jega.

Wasu daga cikin manyan baki da suka halarci bikin sun hada da Alhaji Abubakar Kana-Zuru, shugaban jam’iyyar APC na jihar; Alhaji Sani Zauro, shugaban kungiyar dattawan APC na jiha; da Alhaji Faruk Musa-Yaro, Mataimakin Gwamnan Jihar.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gobara na cigaba da lakume wasu yankunan Turai

Gobarar daji na ci gaba da ruruwa a sassan...

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...

Gwamnati za ta gina titin jirgi a jihohi shida

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta haɗa gwiwa da...

Tinubu ya na cikin koshin lafiya – Farouk Adamu Aliyu

Tsohon ɗan majalisar wakilai daga jihar Jigawa, Faruk Adamu...

Amurka ta saka ladan dala miliyan biyar a kamo jagoran ‘yandaban Haiti

Amurka ta sanya dala miliyan biyar a matsayin lada...

Gwamnati ta janye karar da ta shigar kan Fasinjar jirgin Ibom

Gwamnatin Tarayya ta janye ƙarar da ta shigar kan...

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...
X whatsapp