fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: PDP ta dakatar da shugabanta a Zamfara

Date:

Jam’iyyar PDP reshen jihar Zamfara ta sanar da dakatar da Kanar Bala Mande mai ritaya har sai an kammala bincike kan zargin da ake masa.

A cewar sanarwar da sakataren yada labaran jam’iyyar na jihar, Abba Bello ya fitar ranar Laraba a Gusau, an dakatar da shugaban ne saboda wasu ayyukan da suka saba wa jam’iyyar.

“Hakan ya zama dole saboda shugaban jam’iyyar na gudanar da harkokin jam’iyyar ba tare da sa hannun kwamitin gudanarwa na jihar ba.”

Sanarwar ta kara da cewa, matakin nasa ya sabawa sassa daban-daban na kundin tsarin mulkin PDP.

“Ya zama dole a dakile cin zarafi da kuma karya dokokin tafiyar da jam’iyyar.

“Dakatar da aka yi na tsawon wata daya ne, wannan yana da kyau a baiwa kwamitin aiki damar kafa kwamitin bincike kan zargin”.

“Bisa abubuwan da suka gabata, mataimakin shugaban shiyyar Kaura Namoda, Malam Ali Namoda zai kula da ayyukan jam’iyyar na tsawon lokacin da aka dakatar da shi”.

Bello ya ci gaba da cewa, kwamitin aiki na jihar ya kaddamar da kwamitin bincike domin gudanar da bincike kan wannan zargi.

Mambobin kwamitin sun hada da Ahmed Sani Kaura a matsayin shugaba, Bala Zurmi Member, Sanin Baba memba, Abdulhadi Ahmed memba, Suwaiba Bako Memba Abul Mustapha, da Barr. Ibrahim Jibril zai zama Sakatare.

dailypost news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp