Misis Ifeoma Kalu, matar tsohon gwamnan jihar Abia, Sanata Orji Kalu ta mutu.
Dan majalisar tarayya ya tabbatar da faruwar lamarin a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook ranar Litinin.
Bulaliyar majalisar dattawan ya ce Ifeoma, wacce ta rasu tana da shekaru 61, mace ce mai nagarta da ta himmatu wajen bautar Allah da kuma bil’adama.
Kalu ya rubuta, “Cikin zuciya da zafi, muna sanar da rasuwar Misis Ifeoma Ada Kalu mai shekaru 61.
“Mace ce mai nagarta wacce ta himmantu ga bautar Allah da bil’adama.
“An shirya gudanar da wani taron tunawa da girmamawarta a Amurka.”