fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Masu ruwa da tsaki a PDP sun buƙaci shugaban jam’iyyar ya yi murabus

Date:

Sakamakon fitowar tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar a matsayin dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, wasu masu ruwa da tsaki na jam’iyyar na neman Sanata Iyorchia Ayu, shugaban jam’iyyar na kasa ya yi murabus.

Daily Independent ta rawaito cewa, wasu masu ruwa da tsaki na jam’iyyar na yin wannan bukata ne saboda yadda jam’iyyar PDP ta yi shiyya-shiyya. Sun yi zargin cewa shugaban kasa da dan takarar shugaban kasa ba za su iya fitowa daga shiyya daya ba.

Hakazalika sun bayyana cewa a ganawar da suka yi da gwamnonin PDP wanda ya kai ga zabensa a matsayin shugaban kasa, Ayu ya sanya hannu kan yarjejeniyar cewa, idan dan takarar shugaban kasa ya fito daga Arewa zai yi murabus daga mukaminsa don ba da damar sabon shugaban kasa daga jam’iyyar.

Ayu ya ce a shirye ya ke ya sadaukar domin ganin jam’iyyar PDP ta samu nasara a 2023 kuma zai sauka daga mulki idan jam’iyyar ta bukaci ya yi hakan, yayin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan ya zama shugaban jam’iyyar na kasa.

Wani tsohon minista daga Kudu-maso-Kudu, wanda ke jagorantar zanga-zangar neman Ayu ya yi murabus, ya ce, jam’iyyar za ta fara yunkurin ganin Ayu ya mutunta yarjejeniyar kuma ya yi murabus.

national tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp