fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Masu garkuwa sun yi awon gaba da mutane da dama a Abuja

Date:

An yi garkuwa da wasu mutanen da ba a tantance adadinsu ba a Abuja, lokacin da wasu ‘yan bindiga suka kai hari a cikin gidajensu da sanyin safiyar ranar Litinin.

Gidan da aka kai harin yana unguwar Gwarinpa ne a Abuja, babban birnin tarayya, inji rahoton Naija News Hausa.

‘Yan bindigar wadanda aka ce sun zo ne da wasu makamai da suka hada da baka, kibau, da adduna, sun gudanar da aikin ne a yankin tsakanin karfe daya na safe zuwa karfe hudu na safe.

Da yake bayyana hakan, wani mazaunin garin mai suna Mohammed ya shaida wa Aminiya ta wayar tarho cewa, ‘yan bindigar sun samu shiga Estate ne, bayan Efab Queens da ke 6th Avenue, Gwarinpa.

Da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, DSP Josephine Adeh, ta bayyana faruwar lamarin a matsayin na fashi da makami ba wai na garkuwa da mutane ba.

Ta kara da cewa, an tattara jami’an ‘yan sanda zuwa wurin da lamarin ya faru tare da yin alkawarin bayyana sakamakon binciken su ga jama’a da zarar an samu karin haske.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp