fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: INEC ta tabbatar da Machina maimakon Lawan

Date:

Hukumar zabe mai zaman kanta ta tabbatar da Bashir Machina a matsayin wanda ya lashe zaben fidda gwani na jam’iyyar All Progressives Congress mai wakiltar mazabar Yobe ta Arewa.

Wani tabbataccen kwafin rahoton INEC na ranar 28 ga Mayu, 2022, zaben ya nuna Machina ya samu kuri’u 289 cikin wakilai 300, wanda hakan ke tabbatar da ikirarin da ‘yan siyasar ke yi na cewa, shi ne ya lashe zaben fidda gwani kuma ya yi takara a bisa doka.

Takardar wacce ofishin zabe ta tabbatar a ranar 23 ga watan Yuni, 2022, ba ta ambaci Ahmad Lawan ba, shugaban majalisar dattawan da ya yi ta kokarin karɓe wa Machina aiki tare da shugaban jam’iyyar na kasa Abdullahi Adamu.

Adamu ya sanya sunan Lawan a matsayin dan takarar jam’iyyar APC a zaben Sanatan Yobe ta Arewa da aka shirya gudanarwa a watan Fabrairun 2023, yana mai cewa an gudanar da zaben fidda gwani a asirce inda ake zargin Lawan ya yi nasara.

Ko da yake Machina ya samu shaidar lashe zaben, amma har yanzu yana sa ran za a kara gwabzawa lokacin da INEC za ta tsayar da ‘yan takarar da za su tsaya takara a jam’iyyun siyasa daban-daban a makonni masu zuwa. INEC ta ce ba ta da hurumin zabar dan takara a zabe, duk da cewa tantance ta ya zama dole don tabbatar da an gudanar da zabe.

Lawan ya fara yunkurin kwace tikitin ne daga hannun Machina, bayan ya sha kaye a babban taron jam’iyyar da ke mulki, wanda Bola Tinubu ya samu nasara a ranar 8 ga watan Yuni.

mmm.nnn.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...

Wike ya caccaki Rotimi a kan jam’iyyar ADC

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya caccaki tsohon...

Tsige ni daga mukamin Wazirin Gaya ba a kan doka ba ne – Usman Alhaji

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya...

Gini mai bene uku ya danne Mutane a jihar Legas

Wani gini mai bene uku ya rufta a unguwar...

Kotu ta daure Matashi dan Tiktok da ya ke sanya rigar mama

Wata kotu a jihar Kano, ta yanke wa wani...

Peter Obi ka gaggauta ficewa daga jam’iyyar mu nan da awa 48 – Labour Party

Bangaren jam’iyyar Labour da Julius Abure ke jagoranta, ya...
X whatsapp