Hadimin shugaban kasa Muhammadu Buhari, Bashir Ahmaad ya tabbatar da sauya shekar Goodluck Jonathan zuwa jam’iyyar All Progressives Congress, APC.
Bashir ya tabbatar da hakan ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter a ranar Alhamis yayin da yake mayar da martani ga masu shakkar hasashen da ya yi a baya na cewa tsohon shugaban kasar zai sauya sheka zuwa jam’iyya mai mulki.
A sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter ya ce: “Lokacin da na bayar da labarin shigowar tsohon shugaban kasa Jonathan jam’iyyarmu, magoya bayansa da ba su sani ba sun zage ni cewa hakan ba zai taba faruwa ba ko da a mafarki.
“Ya kamata su sani cewa mun san wani abu da ba su sani ba kuma ba duk abin da aka shirya da aiwatar da shi a shafukan sada zumunta ba.”
Idan dai za a iya tunawa, an ce wata kungiyar arewa ce ta siya wa tsohon shugaban kasa Jonathan fom din tsayawa takara da fam miliyan 100 na jam’iyya mai mulki a ranar Litinin.