Shugaban hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, Abdulrasheed Bawa, ya bayyana cewa an bayar da belin tsohon gwamnan jihar Anambra, Willie Obiano.
Obiano, wanda ake tuhumarsa da laifin almundahanar Naira biliyan 42, ya kasance a hannun EFCC, tun ranar Alhamis lokacin da aka kama shi a filin jirgin sama na Murtala Muhammed da ke jihar Legas, a lokacin da yake yunkurin tafiya kasar Amurka.
Amma da yake zantawa da manema labarai a wajen taron shekara-shekara karo na 5 na kungiyar masu yaki da cin hanci da rashawa a Afirka ta Yamma a Abuja ranar Litinin, Bawa ya bayyana cewa hukumar na jiran ya kammala belinsa.
Da aka tambaye shi dalilin da ya sa hukumar ta tsare tsohon gwamnan a hannun ta, fiye da wa’adin da tsarin mulki ya ba ta, Bawa ya ce, “Babu wani abu na siyasa game da tsare tsohon gwamnan jihar Anambra, Wille Obiano. An bayar da belinsa.”
Shugaban EFCC bai bayyana cikakken bayanin belin ba.