fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: EFCC ta bayar da belin Obiano

Date:

Shugaban hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, Abdulrasheed Bawa, ya bayyana cewa an bayar da belin tsohon gwamnan jihar Anambra, Willie Obiano.

Obiano, wanda ake tuhumarsa da laifin almundahanar Naira biliyan 42, ya kasance a hannun EFCC, tun ranar Alhamis lokacin da aka kama shi a filin jirgin sama na Murtala Muhammed da ke jihar Legas, a lokacin da yake yunkurin tafiya kasar Amurka.

Amma da yake zantawa da manema labarai a wajen taron shekara-shekara karo na 5 na kungiyar masu yaki da cin hanci da rashawa a Afirka ta Yamma a Abuja ranar Litinin, Bawa ya bayyana cewa hukumar na jiran ya kammala belinsa.

Da aka tambaye shi dalilin da ya sa hukumar ta tsare tsohon gwamnan a hannun ta, fiye da wa’adin da tsarin mulki ya ba ta, Bawa ya ce, “Babu wani abu na siyasa game da tsare tsohon gwamnan jihar Anambra, Wille Obiano. An bayar da belinsa.”

Shugaban EFCC bai bayyana cikakken bayanin belin ba.

natforce 
latest news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp