Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, yana jagorantar wata ganawa da wasu ministoci da shugabannin hukumomin tsaro a fadar gwamnati da ke Abuja.
Taron wanda aka shirya gudanarwa tun ranar Talata, 19 ga Afrilu, 2022, ya zo mako guda bayan shawarar da Majalisar Jiha ta bayar.
Cikin wadanda suka halarci taron akwai mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo; Sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha; Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari; da mai baiwq shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Manjo Janar Babagana Monguno (mai ritaya).
Ministocin da suka halarci taron sun hada da ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola; Ministan Harkokin Waje, Geoffrey Onyeama, da Ministan Tsaro, Manjo Janar Bashir Magashi (mai ritaya).
Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da babban hafsan soji, Laftanar-Janar. Farouk Yahaya; Babban Hafsan Sojan Ruwa, Vice-Adm. Awwal Gambo; Shugaban hafsan sojin sama Air Marshal Isiaka Amao da babban hafsan hafsoshin tsaro Janar Lucky Irabor wanda ya samu wakilcin.