Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Ribas a safiyar ranar Litinin, sun harba barkonon tsohuwa kan masu zanga-zangar a Fatakwal, babban birnin jihar.
Masu zanga-zangar dai sun taru ne a filin shakatawa na Isaac Boro lokacin da jami’an suka kutsa kai cikin yankin.
Kungiyar Take It Back Movement ce ta shirya zanga-zangar kan ayyana dokar ta-baci a jihar Ribas.
‘Yan sanda sun tarbi mambobin kungiyar ne a lokacin da suka taru a wurin zanga-zangar da misalin karfe 9:00 na safe.
“Babu wanda zai iya gaya mana inda ba za mu taru ba, mu mutanen Rivers ne,” Channels TV ta ruwaito matasa masu zanga-zangar suna yiwa ‘yan sanda ihu.
Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta shawarci masu shirya zanga-zangar da su ajiye tsare-tsarensu.