fidelitybank

Da yuwar Wike ya yar da kwallon mangwaro ya huta da kuda

Date:

Rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar PDP ya sake daukar wani sabon salo a ranar Talata yayin da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC mai mulki, Bola Tinubu, ya gana da wasu gwamnonin PDP ciki har da Nyesom Wike na jihar Rivers a birnin Landan.

An tattaro cewa gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo da takwaransa na jihar Abia, Dr Okezie Ikpeazu da sauran jiga-jigan jam’iyyar PDP daga sansanin gwamna Wike ne suka halarci taron.

DAILY POST ta tattaro cewa Wike da wasu jiga-jigan jam’iyyarsa ta PDP ciki har da Gwamna Samuel Ortom sun tafi kasar Ingila domin yin wannan ganawar.

Ku tuna cewa bayan shan kaye da ya yi a zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Gwamna Wike ya sha fama da yakin da ake yi da dan takarar jam’iyyar, Atiku Abubakar.

Kokarin da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar ke yi na ganin an warware sabanin da ke tsakaninsu ya ci gaba da kawo cikas, yayin da sansanin Wike ya bukaci shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Sanata Iyorchia Ayu ya yi murabus.

A cewar rahotanni, taron da aka yi a Landan ya ta’allaka ne kan bukatar Wike sansanin su goyi bayan burin shugaban kasa na Tinubu.

yola news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

INEC za ta fitar da sabbin ƙa’idojin duba sakamakon zaɓe

A shirye-shiryen da take yi gabanin babban zaɓen Najeriya...

Isra’ila ta amince da sharuÉ—É—an yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce Isra'ila ta amince...

Buhari ba zai taÉ“a cin amanar Tinubu ba – Garba Shehu

Tsohon babban mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai...

Mutane 207 ne suka mutu a ambaliyar Neja – NSEMA

Darakta Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta...

Jiga-jigan jam’iyyar PDP za su sauya sheÆ™a don tunkarar APC a 2027

Wasu jiga-jigan jam'iyyar PDP da suka hada da tsohon...

Za a Æ™addamar da jam’iyyar hammaya da za ta tunkari APC

Gamayyar jam'iyyun adawa a ranar Talata, ta amince da...

Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram Takwas a jihar Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta sun kashe aƙalla...

Sauya sunan Kwaleji a Oyo ya fusata Dalibai

ÆŠaliban kwalejin fasaha ta Ibadan sun gudanar da zanga-zanga...

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Dantata

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta'aziyya...

Trump ba shi da hankali ko tunani a kan harajin sa – Elon Musk

Tsohon mai ba shugaban Amurka Donald Trump shawara kan...

Dangote ya rage man fetur lita 840

Matatar man Dangote ta rage farashin litar man fetur...
X whatsapp