Rundunar sojin Isra’ila IDF ta ce ta ƙaddamar da hari kan cibiyoyin ƙera makami mai linzami da na nukiliya a Iran yayin da Shugaba Donald Trump ke tattauna yiwuwar sojojin Amurka su shiga yaƙin.
Hakan na nufi da cewa akwai zaɓi uku ga Shugaba Trump ko dai ya shiga yaƙin, ko ya tsame kansa ko kuma ya nemi a tattauna.
Rundunar IDF ta ce an aika jiragen yaƙin Isra’ila sama da hamsin a rana ta shida na yaƙin.
Sai dai Amurka ce kaɗai take da ikon kai wa cibiyoyin nukiliyar Iran na ƙarƙashin ƙasa hari.
Rahotanni na cewa an samu rarrabuwar kai a majalisar tsaron Amurka kan matakin da ya fi dacewa ƙasar ta ɗauka amma Trump ya yi wata tattaunawa ta waya da Firaiministan Isra’ila.