Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) kuma tsohon ministan sufuri, Rt. Hon. Chibuike Rotimi Amaechi, ya ce, ba shi da masaniya kan duk wani yunkuri da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu zai yi na sasanta shi da wani jigo a jam’iyyar a jihar Ribas, Sanata Magnus Ngei Abe.
Abe ya taba zama sakataren gwamnatin jihar Ribas a lokacin Amaechi na farko kuma ya wakilci gundumar Ribas ta kudu maso gabas a majalisar dokokin kasa.
Amaechi, wanda ya zanta da manema labarai a sakatariyar jam’iyyar APC ta jihar da ke Fatakwal, babban birnin jihar Ribas a ranar Asabar, ya ce; “Ban san cewa akwai shirin Asiwaju Ahmed Bola Tinubu na sasanta ni da Magnus Abe.”
Tsohon Ministan wanda ya kai ziyararsa ta farko a jihar, tun bayan da Tinubu ya rasa tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC kimanin makonni hudu da suka gabata, ya ce yana kokarin sasanta duk wasu masu fada a ji a cikin jam’iyyar.
Ya ce: “Duk lokacin da kuka sami canji, tabbas za ku sami sabani. Ina magana ne game da abin dake faruwa a tsakaninmu. A cikin mako ɗaya, biyu, uku, za mu iya warware matsalolin. Batun dan takarar gwamna ba ne. Ina bukatar in zauna da su, in ce, ko za mu iya ci gaba.”