fidelitybank

Da yiwuwar Buni ne zai jagoranci babban taron APC

Date:

 

 

Ga dukkan alamu, Shugaban Kwamitin Riƙo na Jam’iya mai mulki APC kuma Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni ne zai jagoranci babban taron APC na ƙasa a ranar 26 ga watan Maris.

Jaridar Punch ta jiyo cewa Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya umarci Buni ɗin da ya jagoranci taron, amma ya masa zazzafan kashedi cewa ba za a ƙara ɗage ranar yin Babban taron jam’iyar na ƙasa ba.

Majiyoyi sun shaida wa Punch cewa Buhari ya ɗauki wannan matakin ne bayan ganawa da ya yi da wasu jiga-jigan jam’iyar a Landan.

Da ga cikin waɗanda su ka baiwa Buharin shawarar ɗaukar wannan matakin akwai Antoni-Janar kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, wanda ya nuna wa shugaban ƙasar illar da za a iya samu ta ɓangaren Shari’a.

Haka-zalika an jiyo cewa, bayan da a yanzu shugaban ƙasar ya nuna ba shi da wani ɗan takara a zaben shugaban jam’iyar na dindindin, yanzu gurbin ya zamto a bude, inda kowa zai iya nema.

Hakan kuma, in ji majiyoyi, ya nuna rashin tabbas a kan rabon muƙamai na shiyya-shiyya da jam’iyar ta fitar a makon da ya gabata.

Haka kuma a ganawar ta birnin Landan, Buhari ya musanta bada umarnin cire Buni da kuma maye gurbinsa da Gwamna Abubakar Sani Bello kamar yadda Gwamna Nasir El-Rufai ya faɗa.

Sannan jaridar ta jiyo cewa gargaɗin da Buhari ya yi ya sanya yawancin gwamnonin da ba sa yin Buni sun maida wukar ta su.

naija legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp