fidelitybank

Da wuya a gano mai rai a cikin wanda kasa ta ruftawa a Neja

Date:

Mahukunta a Najeriya sun ce babu tsammanin gano ko da mutum guda da rai cikin masu hakar ma’adanan da kasa ta ruftawa a jihar Neja.

Wannan lamari ya faru ne a yankin Galkogo na jihar sama da sati uku ke nan da suka gabata

Honorable Yussif Shu’aibu Mani Sule Jaa, shugaban kungiyar ma’aikatan hakar ma’adanai ta kasa a Najeriya reshen jihar Naija ya ce zai yi wuya a iya tantance adadin mutanen da kasa ta danne a ibtila’in kasancewar mutumin da ake tunanin yana da bayanai game da ma’aikatan da ake aiki a wurin shi ma yana cikin wadanda lamarin ya rutsa da su.

Sai dai a cewarsa, bayanai sun nuna mutanen da lamarin ya rutsa da su sun zarce 30.

Jami’in ya kara da cewa shawarar da suka bayar duba da cewa lokaci na kurewa shi ne a yi kokarin zakulo gawarwakin daga karkashin kasa don yan uwansu su iya shaida su, “wadanda za a iya masu sallah, a yi masu.” in ji shi.

A iya saninsa a cewarsa, ba ya tsammanin an yi wani abu don fitar da mutanen daga inda suke ba.

Ya bayyana cewa “dutse ne ya rushe da su a cikin kogon da suke ciki, ka san aikin ma’adinai, rami aka yi a cikin dutsen, sannan saman an barshi, kasan kuma an riga an bude, da ya tashi rushewa, sai ya rushe daga sama ya rufe da su ciki.

Ya kara da cewa “kusan kwana ashirin da wani abu a ce mutum na kunshe a rami – ba abinci ba ruwa ba iska, tana iya daurowa a bude a samu wasu da rai, kasan Allah Sarkin iko.” kamar yadda ya ce.

sspdf news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp