fidelitybank

Da sauran mu har yanzu wajen kafa ‘yan sandan jihohi – Sufeta Kayode

Date:

Babban spetan ƴan sanda na kasa, Kayode Egbetokun, ya ce ƙasar ba ta kai ta kafa rundunar ƴan sandan jiha ba duk da ƙalubalen tsaro da ƙasar ke fuskanta.

Ya bayyana haka ne ranar Litinin yayin wani taron tattaunawa game da kafa rundunar ƴan sandan jiha da aka gudanar a Abuja, babban birnin ƙasar da aka yi wa taken “Hanyoyin samun zaman lafiya: Sake fasalin ƴan sanda a Najeriya”.

Babban Spetan ƴan sandan ya ce har yanzu Najeriya ba ta kai lokacin da za ta kafa rundunar ƴan sandan jihohi ba, in ji shi wanda ya samu wakilcin AIG Ben Okolo a taron da kakakin majalisar wakilan Najeriya, Tajuddeen Abbas ya shirya.

Babban spetan ya ce akwai yiwuwar wuce gona da iri daga gwamnatocin jihohi.

“Gwamnonin jihohi na iya amfani da ƴan sandan domin buƙatarsu ta siyasa ko ta ƙashin kai tare da murƙushe haƙƙoƙin bil adama da tsaro.”

Sai dai ya bayar da shawarwari na yadda za a inganta ayyukan ƴan sanda wajen haɓaka tsaro a ƙasar.

“Da farko, hukumar tsaron Civil Defence da hukumar kare afkuwar haɗura su kasance sashe aƙarƙashin rundunar ƴan sandan Najeriya,” in ji shi.

A cewar babban spetan, akwai buƙatar a ƙara yawan jami’an tsaron da ake ɗauka aiki duk shekara. Da kuma basu horo, abin da ya ce na da muhimmanci wajen tabbatar da tsaro a Najeriya.

A taron da ya samu halartar manyan jami’ai a Najeriya, tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan yana ganin duk da ƙalubalen da ake fuskanta, kafa rundunar ƴan sandan jihohi a Najeriya abu ne na dole.

Ya ce ƙaruwar sace-sacen mutane da sauran laifuka ya sa kafa rundunar ƴan sandan jihohi ya zama wajibi a halin da ake ciki a Najeriya.

Ba ya ga Jonathan, taron ya samu halarta mataimakin shugaban ƙasa Kassim Shettima inda ya bayyana ƙudirin shugaba Bola Tinubu na inganta ayyukan ƴan sanda a ƙasar.

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp