fidelitybank

Da sauran mu har yanzu wajen kafa ‘yan sandan jihohi – Sufeta Kayode

Date:

Babban spetan ƴan sanda na kasa, Kayode Egbetokun, ya ce ƙasar ba ta kai ta kafa rundunar ƴan sandan jiha ba duk da ƙalubalen tsaro da ƙasar ke fuskanta.

Ya bayyana haka ne ranar Litinin yayin wani taron tattaunawa game da kafa rundunar ƴan sandan jiha da aka gudanar a Abuja, babban birnin ƙasar da aka yi wa taken “Hanyoyin samun zaman lafiya: Sake fasalin ƴan sanda a Najeriya”.

Babban Spetan ƴan sandan ya ce har yanzu Najeriya ba ta kai lokacin da za ta kafa rundunar ƴan sandan jihohi ba, in ji shi wanda ya samu wakilcin AIG Ben Okolo a taron da kakakin majalisar wakilan Najeriya, Tajuddeen Abbas ya shirya.

Babban spetan ya ce akwai yiwuwar wuce gona da iri daga gwamnatocin jihohi.

“Gwamnonin jihohi na iya amfani da ƴan sandan domin buƙatarsu ta siyasa ko ta ƙashin kai tare da murƙushe haƙƙoƙin bil adama da tsaro.”

Sai dai ya bayar da shawarwari na yadda za a inganta ayyukan ƴan sanda wajen haɓaka tsaro a ƙasar.

“Da farko, hukumar tsaron Civil Defence da hukumar kare afkuwar haɗura su kasance sashe aƙarƙashin rundunar ƴan sandan Najeriya,” in ji shi.

A cewar babban spetan, akwai buƙatar a ƙara yawan jami’an tsaron da ake ɗauka aiki duk shekara. Da kuma basu horo, abin da ya ce na da muhimmanci wajen tabbatar da tsaro a Najeriya.

A taron da ya samu halartar manyan jami’ai a Najeriya, tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan yana ganin duk da ƙalubalen da ake fuskanta, kafa rundunar ƴan sandan jihohi a Najeriya abu ne na dole.

Ya ce ƙaruwar sace-sacen mutane da sauran laifuka ya sa kafa rundunar ƴan sandan jihohi ya zama wajibi a halin da ake ciki a Najeriya.

Ba ya ga Jonathan, taron ya samu halarta mataimakin shugaban ƙasa Kassim Shettima inda ya bayyana ƙudirin shugaba Bola Tinubu na inganta ayyukan ƴan sanda a ƙasar.

latest nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin...

Ƴansanda sun kama ƙasurgumin ɗanbindiga a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta ce, jami'an ta sun...

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...

Rasha tarnaki ce a wajen Tarayyar Turai – Jamus

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa...

Amurka ba ta goyon bayan Isra’ila a harin Syria – Trump

Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da...

Tinubu zai zo Kano ta’aziyyar Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau...
X whatsapp