Mijin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, Babban Cif Emmanuel, ya goyi bayan matarsa kan zargin da ake yi wa Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Godswill Akpabio.
A wata sanarwa a ranar Asabar, Uduaghan ya tabbatar da cewa Akpabio ya nemi yin baɗala da matarsa, Natasha.
A cewarsa, shi da kan sa ya hadu da Akpabio ne domin ya daina cin zarafin matarsa.
Ya kara da cewa duk da yarjejeniyar da Akpabio ya yi na mutunta matarsa, lamarin ya ci tura.
“Mata ta ta ba ni labarin yadda ta yi mu’amala da Shugaban Majalisar Dattawa, wanda na dauka a matsayin abokin iyali.
“A matsayina na mayar da martani, na tunkari lamarin da matuƙar balaga da alhaki, domin aikina ne a matsayina na shugaban gargajiya wanda ke mutunta ikon da aka kafa da kuma kiyaye ƙa’idodin iyali don samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.
“Ni da kaina na gana da Shugaban Majalisar Dattawa, kuma na roke shi cikin girmamawa da ya kara wa matata ladabi da girmama da ta kamace mu tare da girmama zumuncin da ke tsakaninmu. Mun samu fahimtar juna kuma mun amince da a warware matsalar cikin ruwan sanyi.
“Amma duk da wannan yarjejeniya, matata ta ci gaba da bayyana damuwarta game da tsangwamar da ta sha daga shugaban majalisar dattawa.
“Ina da bangaskiya marar kaskantar da kai ga amincin matata kuma na himmatu sosai ga aurenmu, wanda ya dangana cikin ƙauna, tausayi, da mutunta juna. Ba zan taɓa musayar ta da komai ba, domin ita ce mafi girman farin cikin rayuwata.
“A yanzu ina kira ga Majalisar Dattawan Tarayyar Najeriya da Shugaban Majalisar Dattawa cikin mutuntawa da su girmama matata ƙaunataccena da mutuncin da ta kamace ta da gaske yayin da hukumomin da abin ya shafa da kuma kotu ke tantance al’amuran da ke faruwa,” in ji shi.
Hakan na zuwa ne bayan Natasha, yayin wata hira da ta yi da gidan talabijin na Arise a ranar Juma’a, ta zargi Akpabio da yin lalata da ita.
Tun da farko, DAILY POST ta ruwaito cewa matar Akpabio, Unoma, ta yi watsi da zargin Natasha a kan mijinta.