fidelitybank

Da kaina na kara makin jarabawar JAMB – Daliba Mmesoma

Date:

Yarinyar nan da ake zargi da kara wa kanta maki a jarrabawar JAMB ta amince cewa da kanta da sauya sakamakon jarrabawar.

Ejikeme Mmesoma mai shekarar 19, wadda tsohuwar ɗaliba ce a makarantar ‘Anglican Girls’ Secondary School’ a jihar Anambra, ta bayyana yadda ta kara wa kanta maki a takardar sakamakon jarrabawar.

A ‘yan kwanakin nan, batun ya janyo ce-ce-ku-ce, tun bayan da hukumar da ke shirya jarrabawar ta karyata makin da dalibar ta yi ikirarin samu a jarrabawar.

Ita dai hukumar JAMB ta ce dalibar ta samu maki 249, saɓanin maki 362 da take ikirarin samu, to sai dai a lokacin ɗalibar ta kafe cewa sakamakon da take ikirari shi ne na gaskiya.

Lamarin da ya sa gwamnan jihar Anambra Charles Soludo ya kafa wani kwamiti domin gudanar da bincike kan lamarin.

Kwamitin ya gayyaci ɗalibar da shugabar makarantar da kuma jami’an hukumar JAMB domin jin bahasin kowanne ɓangare.

Hukumar ta JAMB ta ce sakamakon da ɗalibar ke ikirarin samu wanda ke dauke da maki 362 sakamako ne na bagi, ba na gaskiya ba.

Haka kuma JAMB din ta bayyana yadda Ejikeme Mmesoma ta yi ta yunkurin neman samakamon jarrabawar tata a shafin hukumar cikin sa’o’i da dama, kuma a duk wadannan lokuta sakamako daya take samu daga hukumar wanda ke nuna cewa ta samau maki 249.

To sai dai Ejikeme Mmesoma ta shaida wa kwamitin cewa ta amince da wanna bayani da hukumar jami’an hukumar ta JAMB suka yi wa kwamitin.

Tana mai cewa da kanta ta kara makin sakamakon jarrabawar tata.

Ta ce ta yi amfani da wayarta wajen sauya sakamakon jarrabawar, kafin ta fitar da takardar sakamakon jarrabawar.

Kwamitin ya yi kokarin gano dalilin ɗalibar na aikata wannan laifi, to sai dai ta ce ba ta da wani kwakkwararn dalili.

Daga ƙarshe kwamitin ya bukaci ɗalibar ta gaggauta neman afuwa bisa wannan laifi da ta aikata, ta hanyar rubuta wasikar neman afuwa ga hukumar JAMB da hukumar Makarantar da ta kammala, sannan zuwa ga gwamnatin jihar Anambar.

Sannan kwamitin ya bukaci dalibar ta je a duba lafiyar kwakwalwarta, tare da yin kira da duka ɗaliban da ke rubuta jarrabawar da su tsaya inda dokokin hukumar ya iyakance musu.

legit nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp