Gwamnatin tarayya ta ba da tabbacin kammala gadar Muhammadu Buhari da aka fi sani da gadar Neja ta biyu da babbar hanyar Legas zuwa Ibadan a shekarar 2022.
Ministan ayyuka da gidaje, Babatunde Fashola ne ya bayyana haka a lokacin da ya ke gabatar da jawabi a taron mako-mako na ministoci, wanda kungiyar sadarwa ta shugaban kasa ta shirya a fadar shugaban kasa, Abuja.
Fashola ya yi bayanin cewa hasashen farkon watan Fabrairu na gadar Neja ta biyu ya gaza saboda tasirin kulle-kullen COVID-19 da zanga-zangar EndSARS, ya kara da cewa aikin ya riga ya kai kashi 91% na kammalawa.
Tattaunawar dai an yi shi ne, domin ba shi damar yin karin bayani kan muhimman hadin gwiwar da ke tsakanin Gwamnatin Tarayya da Gwamnatocin Jihohi wajen aiwatar da wasu manyan sauye-sauye da ma’aikatar da asusun bunkasa ababen more rayuwa na Shugaban kasa (PIDF) ke aiwatarwa.