A ranar 28 ga watan Mayu ne za a buga wasan karshe na gasar kulob mafi shahara a Turai a St Petersburg, wato gasar cin kofin zakarun kungiyoyin nahiyar Turai, sai dai ya gamu da tustu, sakamakon hukumar ta janye daga kasar Rasha saboda afkawa Ukraine.
Bayan wani taro da aka yi ranar Juma’a, Uefa ta tabbatar da cewa, ba za a yi wasan ba a filin wasa na Gazprom Arena.
A maimakon haka hukumar kwallon kafar Turai ta yanke shawarar cewa, za a gudanar da shi a filin wasa na Stade de France da ke birnin Paris.
Uefa ta nuna godiya ga shugaban Faransa Emmanuel Macron saboda goyon bayansa na kashin kansa da kuma jajircewarsa na ganin wasan kwallon kafa mafi daraja a Turai ya koma Faransa a daidai lokacin da ake fama da rikici.