Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, zai kama hanyarsa zuwa London a yau dinnan domin a duba lafiyarsa.
Kakakin shugaban, Femi Adesina a sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter ya ce ana saran Buhari zai koma gida a cikin mako na biyu na watan Nuwamba.
A 2017, Shugaban ya kwashe kwanaki 150 a Burtaniya a wata tafiyar duba lafiyar da ba a bayyana abin da ke damun shi ba.
Buhari ya kara komawa Burtaniya a watan Mayun 2018 domin ganin liktansa, inda ya yi kwana hudu kacal a kasar.
A watan Nuwambar 2020 ne, mai dakin shugaban kasar Aisha Buhari, ta ce akwai bukatar inganta bangaren lafiya a Najeriya domin a rage tafiye-tafiyen neman magani kasashen waje.