Akalla mutane biyar ne ‘yan ta’adda suka kashe a kauyen Manini da ke kusa da Kuriga, a kan hanyar Brinin Gwari zuwa Kaduna.
Kuriga dai ya na karamar hukumar Birnin Gwari ne a jihar Kaduna, wanda ya yi kaurin suna wajen ‘yan fashi.
Shugaban kungiyar Brinin-Gwari Vanguards for Security and Good Governance, Alhaji Ibrahim Abubakar Nagwari, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya bayyana cewa, daga cikin wadanda suka mutu akwai Saifudeen Lawal Isa, wani namijin Brinin-Gwari, mutum daya dan Kuriga da kuma wasu biyu daga Udawa.
A cewarsa, lamarin ya faru ne da misalin karfe 4:30 na yamma, inda ‘yan ta’addan suka bude wuta kan masu ababen hawa a kan babbar hanyar har sau uku, inda ya ce, wasu mata biyu da wasu biyar sun samu raunuka da harsashi.
Ya kara da cewa, “yan ta’addan sun kone kurmus da wata tanka da ke jigilar man fetur zuwa BrininGwari a daidai wurin da ake kashe mutane a Manini.”
A cewarsa, “harin da kashe-kashen da ake yi a yankin na kullum ne”, yana mai jaddada cewa, ya kara dagula zirga-zirgar ababen hawa a kan hanyar Brinin zuwa Gwari zuwa Kaduna.