Wasu da ba a san ko su wane ne ba, sun yi wa Kwamishinan Kimiyya da Fasaha na Jihar Katsina, Dr Rabe Nasir, kisan gilla.
Maharan sun bude wa kwamishinan wuta ne a gidansa da ke Rukunin Gidajen Fatima Shema a garin Katsina a yammacin ranar Alhamis.
Majiyar Aminiya ta ce, “An harbe marigayi Dr. Rabe Nasir ne bayan Sallar La’asar a gidansa da ke Rukunin Gidajen Fatima Shema”.
Kafin zamansa kwamishinan, marigayin Dr. Rabe shi ne mashawarcin gwamna, Aminu Bello Masari na Jihar Katsina a kan Kimiyya da Fasaha.
Dr.a Rabe Nasir haifaffen garin Mani ne a karamar Hukumar Mani ta jihar Katsina, kuma an haife shi ne a watan Oktoban 1960.