A ranar Alhamis ne ‘yan sanda suka harba barkonon tsohuwa a Lekki Tollgate, biyo bayan jerin gwanon da ake ci gaba da yi na tunawa da bikin cika shekaru biyu da harbe-harbe da ya yi sanadiyar rayuka da dama.
Idan dai za a iya tunawa dai shekaru biyu da suka gabata ne aka jefa al’ummar kasar baki daya cikin alhini sakamakon harbe-harbe da aka yi a Lekki Tollgate da ake zargin sojojin Najeriya sun yi na dakatar da matasan da ke zanga-zangar nuna adawa da zaluncin ‘yan sanda.
‘Yan Najeriya da dama ciki har da Amnesty International sun yi zargin cewa jami’an sojojin Najeriya sun harbe masu zanga-zangar.
Matasan dai sun dawo ne a daidai wannan wuri a yau Alhamis, domin tunawa da wannan lamari na bakin ciki.