‘Yan sanda sun samu nasarar daƙile wani harin ‘yan bindiga da suka addabi jihar Katsina, tare da kashe mutane 5 da kuma kwato mutanen da aka sace da dabbobi.
Jaridar Vanguard ta rawaito cewa, ‘yan bindigan sun yi yunkurin kai hari kauyukan Kuru da Dangani a karamar hukumar Musawa jihar Katsina. Sauran abubuwan da ‘yan sandan suka kwato sun haɗa da, bindiga kirar AK-47 guda ɗaya da zaren alburusai da kuma Mota kirar Gulf III.
Mai magana da hukumar ‘yan sanda reshen jihar Katsina, SP Gambo Isa, shi ne ya bayyana hakan, yayin da ya ke holin wa manema labarai wasu daga cikin kayayyakin da aka kwato a Shelkwatarsu ranar Jumu’a.
Ya ce, kwamandan ‘yan sanda na yankin Dutsinma ya samu kiran gaggawa da misalin ƙarfe 1:00 na daren ranar 10 ga watan Janairu, cewa, ‘yan ta’adda da yawa sun farmaki yankin Musawa. Nan take ya jagoranci tawagar yan sanda zuwa hanyar da ake tsammanin za su biyo kusa da kauyen Dangani, suka yi kazamin artabu, yan sanda suka kashe yan ta’adda 5, suka kwato makamai.