fidelitybank

Da Dumi-Dumi: ‘Yan sand sun kama matar da ake zargi da sace yarinya ‘yar shekara 3

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Anambra ta kama wata mata ‘yar shekara 29 mai suna, Miss Chinwendu Umegbaka, bisa zargin sace yaron makwabcinta a Nwawulu Sreet, Okpoko, Onitsha.

An kama wanda ake zargin ne a ranar Asabar da karfe 4:30 na yamma a Okpoko.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Ikenga Tochukwu ya ce, “’Yan sanda sun kama wata Miss Chinwendu Umegbaka ‘yar shekara 29, ‘yar asalin Isinkwo Abaomege a karamar hukumar Onicha ta jihar Ebonyi kan zargin satar yara a Okpoko, Onitsha. , Jihar Anambra.”

A cewarsa, binciken farko na ‘yan sanda ya nuna cewa, wanda ake zargin makwabci ne ga iyayen yaron.

Ya ce, lokacin da aka kama wadda ake zargin, da farko ta musanta cewa, ta san inda yarinyar mai shekaru 3 take.

Kakakin ‘yan sandan ya kuma kara da cewa, da aka ci gaba da yi mata tambayoyi ta amsa laifin satar yaron da nufin sayar da ita.

Sai dai ya bayyana cew,a an dawo da yaron kuma an mika shi ga iyayen sa.

ng news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp