fidelitybank

Da Dumi-Dumi: ‘Yan majalisar dokoki Kano 9 sun koma jam’iyyar NNPP

Date:

Mambobin jam’iyyar PDP tara a majalisar dokokin jihar Kano, sun fice daga jam’iyyarsu zuwa New Nigeria People Party (NNPP).

Sakataren yada labaran Majalisar, Uba Abdullahi ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a ranar Juma’a.

Ya ce ‘yan majalisar da abin ya shafa sun aike da wasika ga shugaban majalisar, inda suka sanar da majalisar cewa sun sauya sheka.

A cewarsa, wasu daga cikin dalilan da ‘yan kungiyar suka bayar na da alaka da rikicin shugabanci a jam’iyyar PDP a matakin jiha da kasa baki daya.

Mambobin da abin ya shafa sun hada da; Isyaku Ali Danja (Mazabar Gezawa), Umar Musa Gama (Mazabar Nassarawa), Aminu Sa’adu Ungogo (Mazabar Ungogo), Lawan Hussain Chediyar ‘Yan Gurasa (Mazabar Dala) da Tukur Muhammad (Mazabar Fagge).

Sauran su ne; Mu’azzam El-Yakub (Mazabar Dawakin Kudu), Garba Shehu Fammar (Mazabar Kibiya), Abubakar Uba Galadima (Mazabar Bebeji) da Mudassir Ibrahim Zawaciki (Mazabar Kumbotso).

A ranar 29 ga watan Afrilu ne majalisar ta sanar da sauya sheka dan majalisar wakilai Salisu Maje Ahmed Gwangwazo daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC sakamakon rikicin cikin gida na jam’iyyar.

PlatinumPost ta rawaito cewa, tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Kwankwaso, ya fice daga jam’iyyar PDP a jihar kwanan nan ya koma jam’iyyar NNPP, inda ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a shekarar 2023 a karkashin jam’iyyar.

sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...

Tawagar Gwamnatin Kano ta shilla Saudiyya zuwa jana’izar Dantata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci...

Tawagar Jami’an gwamnati da Malamai sun tafi jana’izar Dantata

Wata tawaga daga gwamnatin Tarayya, ta isa ƙasar Saudiyya...

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...
X whatsapp