Mambobin jam’iyyar PDP tara a majalisar dokokin jihar Kano, sun fice daga jam’iyyarsu zuwa New Nigeria People Party (NNPP).
Sakataren yada labaran Majalisar, Uba Abdullahi ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a ranar Juma’a.
Ya ce ‘yan majalisar da abin ya shafa sun aike da wasika ga shugaban majalisar, inda suka sanar da majalisar cewa sun sauya sheka.
A cewarsa, wasu daga cikin dalilan da ‘yan kungiyar suka bayar na da alaka da rikicin shugabanci a jam’iyyar PDP a matakin jiha da kasa baki daya.
Mambobin da abin ya shafa sun hada da; Isyaku Ali Danja (Mazabar Gezawa), Umar Musa Gama (Mazabar Nassarawa), Aminu Sa’adu Ungogo (Mazabar Ungogo), Lawan Hussain Chediyar ‘Yan Gurasa (Mazabar Dala) da Tukur Muhammad (Mazabar Fagge).
Sauran su ne; Mu’azzam El-Yakub (Mazabar Dawakin Kudu), Garba Shehu Fammar (Mazabar Kibiya), Abubakar Uba Galadima (Mazabar Bebeji) da Mudassir Ibrahim Zawaciki (Mazabar Kumbotso).
A ranar 29 ga watan Afrilu ne majalisar ta sanar da sauya sheka dan majalisar wakilai Salisu Maje Ahmed Gwangwazo daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC sakamakon rikicin cikin gida na jam’iyyar.
PlatinumPost ta rawaito cewa, tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Kwankwaso, ya fice daga jam’iyyar PDP a jihar kwanan nan ya koma jam’iyyar NNPP, inda ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a shekarar 2023 a karkashin jam’iyyar.