fidelitybank

Da Dumi-Dumi: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da Dan Jarida

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da wani dan jarida mai suna Mista Chuks Onuha a gidansa da ke Umuhu, Ohuhu a karamar hukumar Umuahia ta Arewa a jihar Abia.

Rahotanni sun nuna cewa, Onuha tsohon wakilin jaridar Sun ne a jihar Abia.

Onuha dai yana cin abinci ne tare da iyalansa a daren ranar Talata inda ‘yan bindigar suka kutsa cikin gidansu tare da dauke shi zuwa wani wuri da ba a san ko ina ba, inji rahoton Daily Sun.

An kuma bayyana cewa masu garkuwa da mutanen sun tuntubi iyalansa inda suka bukaci a biya su kudin fansa Naira miliyan 10 a safiyar ranar Laraba.

Matarsa kuma ta tabbatar da faruwar lamarin lokacin da aka tuntube ta a waya. Don haka ta yi kira ga wadanda suka yi garkuwa da su da su saki mijinta ba tare da wani sharadi ba domin kare ‘ya’yansu.

A ranar Talata, SaharaReporters ta kuma ruwaito cewa wasu ‘yan bindiga sanye da kakin ‘yan sanda sun kai hari a babban birnin tarayya Abuja, sun yi garkuwa da mata masu juna biyu uku, yara biyu da wasu 12 a Abuja.

taraba state today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp