Yan bindiga sun sako mutum 75 da suka yi garkuwa da su a ƙauyen Yar Katsina dake ƙarƙashin masarautar Waje a ƙaramar hukumar Bungudu, jihar Zamfar.
Mutanen da suka kubuta sun shiga hannun yan ta’addan ne a manyan hare-hare biyu da suka kai ƙauyen su cikin watanni biyu da suke gabata.
Da farko, yan bindigan sun yi awon gaba da mutane 61, bayan kwanaki 36 kuma suka ƙara yin garkuwa da wasu mutum 15.
Wani mazaunin ƙauyen, Sadiq Sani, ya bayyana cewa, yan ta’ddan sun rike wata mace ɗaya yar shekara 6 a duniya. A cewar Daily Trust.