fidelitybank

Da Dumi-Dumi: ‘Yan bindiga sun sace malamin Coci da matarsa

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun sace Bishop na darikar Anglican, Rabarand Oluwaseun Aderogba da ke Jebba a Jihar Kwara ta Tsakiyar Najeriya tare da matarsa da dirabansa.

Gidan talbijin na Channels TV ya rawaito cewa an sace mutanen ne ranar Lahadi da maraice a kan hanyar Oyo/Ogbomoso da ke Jihar Oyo.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar, Adewale Osifeso, ya tabbatar da sace mutanen a wata sanarwa da ya fitar.

Ya kara da cewa wani mutum mai suna Rabarand Adekunle Adeluwa ne ya kai wa ‘yan sanda labarin sace takwaransa.

A cewar Osifeso, binciken farko ya nuna cewa motar limamin cocin ce ta samu matsala a yayin da suke tafiya daga Yewa da ke Jihar Ogun zuwa Jebba a Jihar Kwara.

Ya kara da cewa an bai wa mataimakin Kwamishinan ‘yan sandan yankin umarnin gano da kuma ceto mutanen.

breaking news in nigeria today punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

JAMB ta amince da maki 150 mafi ƙanƙanta don samun gurbin karatu a jami’o’i

Hukumar shirya jarrabawar shiga Jami'o'i ta Najeriya (JAMB) ta...

ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Ƙungiyar Malaman Jami'o'i ta Najeriya, ASUU da dakatar yajin...

Masu haɗakar ADC na ɓaɓatu ne saboda rashin gwamnati – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umar Radda ya yi...

Ba ruwan Biri da gada a makamin Nukiliya – Shettima

Mataimakin shugaba Najeriya Kashim Shettima ya ce ƙasar za...

An kashe Mutane 70 a jihar Filato

Rahotonni daga jihar Filato na cewa ƴanbindiga sun kai...

Ambaliya ta kashe mutane 100 a Amurka

Hukumomi a jihar Tesxas da ke Amurka sun bayyana...

Tsohon Ministan kuma jigo a PDP ya koma ADC

Tsohon ministan harkokin ‘yan sanda kuma sau uku a...

Trump ya caccaki Elon Musk

Shugaban Amurka Donald Trump ya caccaki tsohon mashawarcinsa, Elon...

Dalilin da ya sa Kwankwaso ya ki shiga jam’iyyar hadaka – Galadima

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...

Obi ba zai taba zama shugaban kasa ba – Wike

Ministan Abuja, Nyesom Wike ya ce, tsohon ɗan takarar...

Ƴansanda sun kama ƴan Ghana 19 da aka yi safararsu a Najeriya

Rundunar ƴansandan Najeriya ta kuɓutar da wasu ƴan Ghana...

Benue da Edo da Bayelsa na fargabar balewar madatsar ruwan Kamaru

Gwamnatocin jihohi uku na cikin shirin ko-ta -kwana, sakamakon...
X whatsapp