fidelitybank

Da Dumi-Dumi: ‘Yan bindiga sun kashe ‘yan sanda 2 da fararen hila 3 Bayelsa

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun kai hari tare da kashe ‘yan sanda biyu, fararen hula uku, tare da jikkata wasu da dama a karamar hukumar Ogbia da ke jihar Bayelsa.

Daily Post ta ruwaito cewa, wasu ‘yan bindiga da har yanzu ba a tantance ko su waye ba sun kai wa wata motar da ke dauke da jami’an ‘yan sanda da wasu fararen hula hari a lokacin da ta fito daga jana’izar wani abokin aikinsu.

A cewar wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Asinim Butswat ya fitar, ya ce, “A ranar 14 ga watan Mayun 2022, da misalin karfe 0745, ‘yan bindiga sun yi wa ‘yan sandan kwanton bauna da ke aiki a Rundunar Ribas, a titin Idema- Otuabagi, karamar hukumar Ogbia, jihar Bayelsa, yayin da yana dawowa daga jana’izar wani abokin aikinsa, marigayi ASP Gilbert Sampson, a Imago Kugbo, jihar Ribas.”

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “’yan bindigar da ake zargin ‘yan bindiga ne sun bude wuta kan motar da ke dauke da jami’an ‘yan sanda da sauran fararen hula. Ana cikin haka an harbe PC Asuo Osuani ‘m’ da Special Constabulary Odeoye Sampson ‘m’, Mista Terry Lucky ‘m’, Jennifer Adejo ‘f’, da Asueroh Tobins ‘f’ har lahira, daga bisani kuma suka mutu, yayin da Insfekta Urere Edwin. Murna Sampson ‘f’ da Reward Sampson ‘f’ sun sami raunukan harsasai kuma suna amsa magani”

leadership newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...

Wike ya caccaki Rotimi a kan jam’iyyar ADC

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya caccaki tsohon...

Tsige ni daga mukamin Wazirin Gaya ba a kan doka ba ne – Usman Alhaji

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya...

Gini mai bene uku ya danne Mutane a jihar Legas

Wani gini mai bene uku ya rufta a unguwar...

Kotu ta daure Matashi dan Tiktok da ya ke sanya rigar mama

Wata kotu a jihar Kano, ta yanke wa wani...

Peter Obi ka gaggauta ficewa daga jam’iyyar mu nan da awa 48 – Labour Party

Bangaren jam’iyyar Labour da Julius Abure ke jagoranta, ya...
X whatsapp