Wasu ‘yan bindiga sun kai hari a kan mutune a titin gaban Makarantar Sakandare ta Gwamnati da ke Kagoro a Jihar Kaduna.
Harin wanda yayi sanadiyar salwantar rayyuka shida, yayin da wasu suka jikkata kamar yadda ganau suka bayyana mai magana da yawun ‘yan sandan Jihar Kaduna, Mohammed Jalige.
Wani ganau, ya kuma tabbatar wa jaridar The Punch rahoton, ya ce, ‘yan bindiga sun taho ne a kan babura sannan suka far wa wadanda suka gani.
Ya ce, mutane shida ne aka tabbatar sun rasu sakamakon harin.
“Yanzu jami’an tsaro suna kwashe daliban makarantar zuwa wani wuri mai tsaro.” Mai magana da yawun yan sandan Jihar Kaduna, Mohammed Jalige, bai amsa kirar da aka masa ba yayin hada wannan rahoton.