fidelitybank

Da Dumi-Dumi: ‘Yan bindiga sun kashe mutum 2 a Jigawa

Date:

An tabbatar da mutuwar mutane biyu, yayin da wasu biyu ke kwance a asibiti, bayan wasu ‘yan bindiga sun kai hari kauyen Garin Gabas da ke karamar hukumar Malam Madori a jihar Jigawa.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Lawal Shiisu, wanda ya tabbatar da hakan ga gidan talabijin na Channels a ranar Asabar, ya ce, ‘yan bindigar sun kuma yi garkuwa da mutum guda.

A cewarsa, “Lamarin ya faru ne a ranar Alhamis da misalin karfe 2:30 inda ‘yan bindiga suka kai hari Garin Gabas a garin Malam Madori inda suka harbe mutum hudu kafin su tafi da wani Musa Malili dan shekara ashirin da biyu.

“Biyu daga cikin hudun da aka harba sun mutu a asibiti yayin da sauran biyun ke karbar magani a asibiti,” ASP Shiisu ya bayyana.

Ya kara da cewa, ‘yan sanda suna yin duk mai yiwuwa don ganin sun kubutar da wanda aka yi garkuwa da shi, ya kuma bukaci ‘yan kasar da su kai rahoton duk wani motsin jama’a da ke damun al’ummarsu.

legitnewsnigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

JAMB ta amince da maki 150 mafi ƙanƙanta don samun gurbin karatu a jami’o’i

Hukumar shirya jarrabawar shiga Jami'o'i ta Najeriya (JAMB) ta...

ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Ƙungiyar Malaman Jami'o'i ta Najeriya, ASUU da dakatar yajin...

Masu haɗakar ADC na ɓaɓatu ne saboda rashin gwamnati – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umar Radda ya yi...

Ba ruwan Biri da gada a makamin Nukiliya – Shettima

Mataimakin shugaba Najeriya Kashim Shettima ya ce ƙasar za...

An kashe Mutane 70 a jihar Filato

Rahotonni daga jihar Filato na cewa ƴanbindiga sun kai...

Ambaliya ta kashe mutane 100 a Amurka

Hukumomi a jihar Tesxas da ke Amurka sun bayyana...

Tsohon Ministan kuma jigo a PDP ya koma ADC

Tsohon ministan harkokin ‘yan sanda kuma sau uku a...

Trump ya caccaki Elon Musk

Shugaban Amurka Donald Trump ya caccaki tsohon mashawarcinsa, Elon...

Dalilin da ya sa Kwankwaso ya ki shiga jam’iyyar hadaka – Galadima

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...

Obi ba zai taba zama shugaban kasa ba – Wike

Ministan Abuja, Nyesom Wike ya ce, tsohon ɗan takarar...

Ƴansanda sun kama ƴan Ghana 19 da aka yi safararsu a Najeriya

Rundunar ƴansandan Najeriya ta kuɓutar da wasu ƴan Ghana...

Benue da Edo da Bayelsa na fargabar balewar madatsar ruwan Kamaru

Gwamnatocin jihohi uku na cikin shirin ko-ta -kwana, sakamakon...
X whatsapp