fidelitybank

Da Dumi-Dumi: ‘Yan bindiga sun kashe mutum 2 a Jigawa

Date:

An tabbatar da mutuwar mutane biyu, yayin da wasu biyu ke kwance a asibiti, bayan wasu ‘yan bindiga sun kai hari kauyen Garin Gabas da ke karamar hukumar Malam Madori a jihar Jigawa.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Lawal Shiisu, wanda ya tabbatar da hakan ga gidan talabijin na Channels a ranar Asabar, ya ce, ‘yan bindigar sun kuma yi garkuwa da mutum guda.

A cewarsa, “Lamarin ya faru ne a ranar Alhamis da misalin karfe 2:30 inda ‘yan bindiga suka kai hari Garin Gabas a garin Malam Madori inda suka harbe mutum hudu kafin su tafi da wani Musa Malili dan shekara ashirin da biyu.

“Biyu daga cikin hudun da aka harba sun mutu a asibiti yayin da sauran biyun ke karbar magani a asibiti,” ASP Shiisu ya bayyana.

Ya kara da cewa, ‘yan sanda suna yin duk mai yiwuwa don ganin sun kubutar da wanda aka yi garkuwa da shi, ya kuma bukaci ‘yan kasar da su kai rahoton duk wani motsin jama’a da ke damun al’ummarsu.

punch newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp