Gwamnatin jihar Neja a ranar Alhamis ta tabbatar da cewa, a ranar Laraba, wasu ‘yan bindiga dauke da makamai sun kai hari a wani wurin hakar ma’adinai da ke kauyen Ajata Aboki ta yankin Erena na karamar hukumar Shiroro.
SIYASAR NIGERIA ta rawaito cewa, wani Manjo Anara da Kaftin Abubakar Samido na daga cikin wadanda sojoji suka jikkata a harin da ‘yan ta’addan suka kai da misalin karfe biyu na rana.
An kashe wasu jami’an tsaro da ba a tantance adadinsu ba ciki har da jami’an ‘yan sanda.
A cewar sanarwar da Emmanuel Umar, kwamishinan tsaro na cikin gida da jin kai na jihar Neja, wata tawagar jami’an tsaro ta hadin gwiwa ta yi da yan ta’addan, “kuma har yanzu ba a tantance adadin wadanda suka mutu daga bangarorin biyu ba”.
An ce an sace wasu ma’aikatan da har yanzu ba a tantance adadin ma’aikata a wurin hakar ma’adinan da suka hada da ‘yan China biyu ba.
“Jami’an tsaro sun hada karfi da karfe domin farautar sauran ‘yan ta’addan yayin da aka kashe wasu daga cikinsu tare da ceto wadanda suka jikkata ciki har da jami’an tsaro da suka samu raunuka daban-daban an kai su asibitin gwamnati da ke jihar domin yi musu magani.