Wasu ‘yan bindiga da har yanzu ba a tantance ko su waye ba, sun kai hari ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC a garin Owerri na jihar Imo.
DAILY POST ta samu labarin cewa harin da aka kai a safiyar ranar Litinin ya yi sanadiyar mutuwar akalla mutane uku.
‘Yan bindigar da suka mamaye ginin da yawan gaske, an ce jami’an rundunar ‘yan sandan Najeriya da wasu jami’an tsaro a yankin sun fatattake su.
A cewar majiyoyin, an kashe uku daga cikin maharan, yayin da aka kama daya daga cikinsu da ransa.
Da DAILY POST ta tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Imo, Michael Abattam, ya yi alkawarin magantu wa a nan gaba.