Wasu ‘yan bindiga sun kai hari a wani masauki da wasu jami’an hukumar yi wa kasa hidima (NYSC) da ke jihar Akwa Ibom.
‘Yan bindigar sun kai hari gidan ne da misalin karfe 1:00 na ranar Laraba, inda suka yi awon gaba da jami’an Corps din kayayyakinsu da ke kan titin Udo Ekong Ekwere da ke wajen Information Drive, Uyo, babban birnin jihar Akw Ibom.
Hukumar NYSC a jihar ta tabbatar da faruwar harin, amma ta musanta rahotannin da ke cewa an yi wa ‘yan NYSC fyade.
Ko’odinetan NYSC na jihar Akwa Ibom Chinyere Ekwe a cikin wata sanarwa da ya fitar ta ce tare da kwamishinan ‘yan sandan jihar, Olatoye Durosinmi, ta ziyarci ‘yan kungiyar domin tantance su nan take,” inji Ekwe.
“A can, an tabbatar da cewa mutum 21 ne suka mamaye wajen. Tattaunawar da jami’an hukumar ya kara nuna cewa barayi ne suka kai musu hari da misalin karfe 1 na safiyar yau.