Wasu ‘yan bindiga sun kai hari gidan shugaban kungiyar ma’aikatan jami’o’i ta kasa (ASUU), reshen jami’ar tarayya ta Gusau (FUGUS), Abdurrahman Adamu.
Rahotanni sun bayyana cewa, an yi garkuwa da mutane shida a harin da aka kai gidan shugaban kungiyar ta ASUU da ke Damba Quarters a Gusau, babban birnin jihar Zamfara.
Wani ma’aikaci, kuma makusancin shugaban ASUU ya shaidawa gidan Talabijin na Channels cewa, ‘yan bindigar sun kai farmaki gidan Adamu ne da sanyin safiyar Laraba, inda suka yi awon gaba da mutane biyar a gidansa
Masu garkuwar sun kuma yi awon gaba da wani makwabcinsu, wanda kuma ma’aikaci ne a sashen bursary na jami’ar.
Majiyar ta kuma bayyana cewa, shugaban na ASUU bai kwana a wannan gidan ba a daren ranar Talata, domin haka ba ya nan a lokacin da aka kai sumamen.
.