A ranar Asabar ne wasu ‘yan bindiga suka kai hari gidan Nnaemeka Obiaraeri, dan takarar majalisar dokokin jihar Imo mai wakiltar karamar hukumar Okigwe a karkashin jam’iyyar Labour Party.
SIYASAR NIGERIA ta samu labarin cewa an kai harin ne da sanyin safiyar yau (Asabar) inda maharan suka kona gidansa tare da ajiye motoci a harabar sa.
A wani bangare bayanin nasa na cewa: “Motoci kirar Hilux guda uku dauke da ‘yan fashi da makasa, sun yi ta kona gidaje tare da raunata mutane ba tare da wani ya hana su ba.
Karanta Wannan: Kaduna Asake take bukata a zaben 2023 – LP
“Ban san wanda na yi wa laifi ba, kuma dalilin da ya sa wani zai kai ni hari don halaka. Ban ci doya ko kifi na kowa ba.
“Wannan wata shaida ce da ke nuna gazawar Gwamnonin APC a Jihar Imo da Aso Rock na Najeriya wajen cika rantsuwar da suka yi na kare rayuka da dukiyoyin ‘yan Najeriya masu bin doka da oda. Gaba daya gazawar gwamnatoci da shugabanni.”