Wasu ‘yan bindiga sama da 10 da ba a san ko su waye ba, sun kai farmaki makarantar ‘yan mata ta Anglican Grammar School, Ozoro, hedkwatar karamar hukumar Isoko ta Arewa a jihar Delta, wurin da ake ci gaba da gudanar da zaben fidda gwani na ‘yan majalisar wakilai na jam’iyyar PDP na mazabar Isoko ta Arewa.
A cewar SaharaReporters, ‘yan bindigar sun taru ne a wurin da kananan motoci kirar Toyota Sienna guda uku, jim kadan bayan an bayyana sakamakon zaben fidda gwani da wakilai da ‘yan takara suka bar wurin. Daga nan ne suka fara harbin iska ba kakkautawa yayin da ‘yan jam’iyyar da magoya bayansu da jami’an tsaro suka yi ta tururuwa zuwa wurin tsira.
An kammala zaben lami lafiya inda mai baiwa jam’iyyar shawara kan harkokin shari’a, Bernard Odion ya lashe zaben da kuri’u 23 inda ya doke dan takara Jude Ogbimi wanda ya samu kuri’a daya. Shugaban karamar hukumar, Emmanuel Egbabor, wanda ya samu kuri’u 8 ne ya zo na biyu.
SaharaReporters ta tattaro cewa, gabanin zaben shugaban karamar hukumar Isoko ta Arewa, Christian Iteire a ranar Juma’a ya yi zargin cewa, ya yi awon gaba da wakilan wucin-gadi tare da yi musu sansani a wani otal domin hana sauran masu son samun damar ganawa da wakilan kafin zaben.