fidelitybank

Da Dumi-Dumi: ‘yan bindiga sun kai farmaki wurin da ake zaben fidda gwani

Date:

Wasu ‘yan bindiga sama da 10 da ba a san ko su waye ba, sun kai farmaki makarantar ‘yan mata ta Anglican Grammar School, Ozoro, hedkwatar karamar hukumar Isoko ta Arewa a jihar Delta, wurin da ake ci gaba da gudanar da zaben fidda gwani na ‘yan majalisar wakilai na jam’iyyar PDP na mazabar Isoko ta Arewa.

A cewar SaharaReporters, ‘yan bindigar sun taru ne a wurin da kananan motoci kirar Toyota Sienna guda uku, jim kadan bayan an bayyana sakamakon zaben fidda gwani da wakilai da ‘yan takara suka bar wurin. Daga nan ne suka fara harbin iska ba kakkautawa yayin da ‘yan jam’iyyar da magoya bayansu da jami’an tsaro suka yi ta tururuwa zuwa wurin tsira.

An kammala zaben lami lafiya inda mai baiwa jam’iyyar shawara kan harkokin shari’a, Bernard Odion ya lashe zaben da kuri’u 23 inda ya doke dan takara Jude Ogbimi wanda ya samu kuri’a daya. Shugaban karamar hukumar, Emmanuel Egbabor, wanda ya samu kuri’u 8 ne ya zo na biyu.

SaharaReporters ta tattaro cewa, gabanin zaben shugaban karamar hukumar Isoko ta Arewa, Christian Iteire a ranar Juma’a ya yi zargin cewa, ya yi awon gaba da wakilan wucin-gadi tare da yi musu sansani a wani otal domin hana sauran masu son samun damar ganawa da wakilan kafin zaben.

nigeria news(punch)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp