Wasu gungun ‘yan bindiga da har yanzu ba a san ko su waye ba a ranar Larabar, sun kai farmaki kan jami’an hukumar shirya jarabawar shiga jami’a ta JAMB a jihar Legas.
Rahotannin da ke isowa Naija News a wancan lokacin, sun tabbatar da cewa maharan da tsakar daren ranar Talata, sun kai hari a otal din Mabila da ke Ikorodu a jihar Legas, inda suka far wa jami’an hukumar jarabawar da fashi da makami.
An ce sun kashe mai gadin otal din ne kafin su kai samame dakunan da ke cikin otal din.
Da yake tabbatar da faruwar harin, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Benjamin Hundeyin, ya shaidawa manema labarai cewa, nan take aka mayar da jami’an hukumar ta JAMB zuwa wani wuri mai tsaro biyo bayan faruwar lamarin.
“Wani Farfesa Odunsi, jami’in hukumar shirya jarabawar shiga jami’a ta JAMB da ya sauka a otal din an yi masa fashin wayoyinsa guda biyu, HP Laptop daya da kudi N20,000.
“Hakazalika, wasu mata biyu jami’an JAMB da suka sauka a otal din, an yi musu fashin wayoyin hannu da kayan kwalliya,” inji shi.
Ma’aikacin kofar otal din a cewar jami’an tsaro ya yi kokarin takaita ‘yan bindigar amma an harbe su a cikin lamarin.