fidelitybank

Da Dumi-Dumi: ‘Yan bindiga sun harbe ‘ya’yan jam’iyar APC a Ebonyi

Date:

Wasu ‘yan bindiga da har yanzu ba a san ko su wanene ba, sun kashe wasu mutane biyu da ake kyautata zaton mambobin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ne a jihar Ebonyi.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne a unguwar Mkpuma Akataka da ke karamar hukumar Izzi a jihar.

Jaridar DAILY POST ta samu labarin cewa taron jam’iyyar APC na gudana ne da yammacin ranar Juma’a a cikin al’umma inda ‘yan bindigar suka far wa wurin inda suka bude wuta.

‘Yan ta’addan wadanda aka ce adadin su biyu ne, sun zo ne a kan babur, inda suka yi sauri su ka tashi, bayan sun kammala aikinsu.

An tabbatar da mutuwar mutane biyu yayin da wasu biyu ke karbar kulawa a asibitin koyarwa na jami’ar tarayya ta Alex Ekwueme da ke Abakaliki.

Kokarin jin ta bakin jami’in hulda da jama’a na ‘yan sanda Chris Anyanwu ya zuwa yanzu bai bayar da amsa ba.

legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp