fidelitybank

Da Dumi-Dumi: ‘Yan bindiga sun harbe ‘yan sanda 4 a Anambra

Date:

Akalla jami’ai hudu ne aka harbe a wani hari da aka kai ofishin ‘yan sandan Atani da ke karamar hukumar Ogbaru a jihar Anambra.

Rahotanni na cewa ‘yan bindigar sun kai harin ne da sanyin safiyar Laraba.
A cewar wata majiya daga Atani, maharan sun isa yankin ne da misalin karfe 1:30 na safiyar Laraba.

Majiyar ta ce, ‘yan sanda hudu da suka hada da mace daya sun rasa rayukansu a harin.

An dai sha kai hare-hare a ofisoshin ‘yan sanda da wasu cibiyoyin gwamnati a Anambra tun bayan da Farfesa Chukwuma Soludo ya hau kujerar gwamna makonni uku da suka gabata.

Soludo ya ci gaba da ba da tabbacin cewa, wadanda ke da alhakin kai hare-haren za a hukunta su ba.

Da yake tabbatar da harin na baya-bayan nan, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Toochukwu Ikenga, ya ce, “‘yan ta’addan sun zo ne da misalin karfe 1:00 na safe, kuma ba mu yi sa’a ba, ‘yan sanda hudu ne suka mutu”.

Ya ce, kwamishinan ‘yan sandan, CP Echeng Echeng, da jin labarin harin, nan take ya tara jami’an rundunar daga sassa daban-daban zuwa yankin.

legit com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp